Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a yau an fara tantance wadanda za su gudanar da gasar kur'ani mai tsarki ta Iskandariyya a Masar wadda zata samu halartar makaranta daga sassan kasar.
Yanzu haka dai an tantance makaranta kimanin 70 wadanda suka samu lasisin wucewa domin shiga cikin gasar.
Wannan gasa ta Iskandariyya ana gudanar da ita ne a kowace shekara akasar Masar, wadda take samun halartar daruruwan makarantan kur'ani da suke karawa da juna.
Za a dauki tsawon kimanin mako guda an agudanar da gasar, kafin zuwa zagaye na karshe, inda za a tantance wadanda suka yi nasara.