Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin Yani Shafaq cewa, a yau firayi ministan kasar Newzealand ta ce ba za ta taba lamuncewa da tsatsauran ra’ayi a kasar ba.
A lokacin da take Karin bayani kan kisan gillar da aka yi wa musulmi a cikin watan Maris da ya gabata, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar musulmi 51 da kuma jikkatar wasu da dama, firayi ministan kasar Newzeland ta sha alwashin kawo karshen irin wannan tsatsauran ra’ayi a kasar.
Gwamnatin kasar dai ta dauki nauyin iyalan wadanda suka rasa rayukansu tare da daukar nauyin karatun ‘ya’yansu, kamar yadda kuma wadanda ba su da shedar zama dan kasa an basu takardun shedar zama ‘yan kasa a hukumance.